An yanke wa mutanen hukuncin ne sakamakon rikicin da aka yi a birnin Minya a bara inda mutane suka musu sannan aka raunata 'yan sanda.
An mika shari'ar zuwa babban Mufti na Masar don ya sake nazarin shari'ar kafin ya yanke hukunci na karshe a watan Yuni.
Ita ce kotun da ta amince da hukuncin kisa a kan 'yan kungiyar 'Yan Uwa Musulmi su kusan 40 a watan da ya gabata.
Sannan kuma aka yanke hukuncin daurin rai-da-rai a kan mutane kusan 500. ABNA.